Luk 24:11-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Su kuwa sai maganan nan ta zama musu kamar zance ne kawai, suka ƙi gaskatawa.

12. Amma Bitrus ya tashi, ya doshi kabarin da gudu. Ya duƙa, ya leƙa a ciki, ya ga likkafanin lilin a ajiye waje ɗaya. Sai ya koma gida yana al'ajabin abin da ya auku.

13. A ran nan kuma sai ga waɗansu biyu suna tafiya wani ƙauye, mai suna Imuwasu, nisansa daga Urushalima kuwa kusan mil bakwai ne.

14. Suna ta zance da juna a kan dukan al'amuran da suka faru.

15. Ya zamana tun suna magana, suna tunani tare, sai Yesu da kansa ya matso, suka tafi tare.

16. Amma idanunsu a rufe, har ba su gane shi ba.

17. Yesu ya ce musu, “Wace magana ce kuke yi da juna a tafe?” Sai suka tsaya cik, suna baƙin ciki.

Luk 24