11. Su kuwa sai maganan nan ta zama musu kamar zance ne kawai, suka ƙi gaskatawa.
12. Amma Bitrus ya tashi, ya doshi kabarin da gudu. Ya duƙa, ya leƙa a ciki, ya ga likkafanin lilin a ajiye waje ɗaya. Sai ya koma gida yana al'ajabin abin da ya auku.
13. A ran nan kuma sai ga waɗansu biyu suna tafiya wani ƙauye, mai suna Imuwasu, nisansa daga Urushalima kuwa kusan mil bakwai ne.
14. Suna ta zance da juna a kan dukan al'amuran da suka faru.
15. Ya zamana tun suna magana, suna tunani tare, sai Yesu da kansa ya matso, suka tafi tare.
16. Amma idanunsu a rufe, har ba su gane shi ba.
17. Yesu ya ce musu, “Wace magana ce kuke yi da juna a tafe?” Sai suka tsaya cik, suna baƙin ciki.