Luk 23:5-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Sai suka fara matsa masa lamba, suna cewa, “Yana ta da hankalin jama'a, yana koyarwa a dukan ƙasar Yahudiya, tun daga ƙasar Galili har zuwa nan.”

6. Da Bilatus ya ji haka, ya tambaya ko mutumin nan Bagalile ne.

7. Da ya ji Yesu a ƙarƙashin mulkin Hirudus yake, sai ya aika da shi wurin Hirudus, don shi ma yana Urushalima a lokacin.

8. Da Hirudus ya ga Yesu, ya yi murna ƙwarai, saboda tun da daɗewa yake son ganinsa, don ya riga ya ji labarinsa, yana kuma fata ya ga wata mu'ujiza da Yesu zai yi.

9. Sai ya yi ta masa tambayoyi da yawa, amma bai amsa masa da kome ba.

Luk 23