Luk 23:16-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.”[

17. A lokacin idi kuwa lalle ne ya sakar musu ɗaurarre guda.]

18. Amma duk suka ɗauki ihu gaba ɗaya, suna cewa, “A yi da wannan ɗin, a sakar mana Barabbas!”

19. (Barabbas shi ne wani mutum da aka jefa a kurkuku, saboda wani tawayen da aka yi a birni, da kuma kisankai.)

20. Sai Bilatus ya sāke yi musu magana, don yana so ya saki Yesu.

21. Amma suka yi ta ƙwala ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”

22. Ya sāke faɗa musu, a faɗa ta uku, “Ta wane hali? Wane mugun abu ya yi? Ai, ban sami dalilin kisa a gare shi ba. Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.”

Luk 23