Luk 21:34-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. “Ku kula da kanku fa, kada zuciyarku ta zarme da yawan shaye-shaye da buguwa, da kuma taraddadin wannan duniya, har ba labari ranan nan ta mamaye ku kamar tarko.

35. Don haka, za ta auka wa mazaunan duniya duk, kowa da kowa.

36. Koyaushe ku zauna a faɗake, kuna addu'a ku sami ikon tsere wa dukan waɗannan al'amura da za su auku, ku kuma tsaya a gaban Ɗan Mutum.”

37. Kullum da rana yakan koyar a Haikali, da dare kuma yakan fita ya kwana a dutsen da ake ce da shi Dutsen Zaitun.

38. Da sassafe kuma dukan mutane sukan zo wurinsa a Haikali su saurare shi.

Luk 21