Luk 20:39-45 Littafi Mai Tsarki (HAU)

39. Sai waɗansu malaman Attaura suka amsa suka ce, “Malam, ka faɗi daidai.”

40. Daga nan kuma ba su yi ƙarfin halin tambayarsa wani abu ba.

41. Amma ya ce musu, “Ƙaƙa za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne?

42. Domin Dawuda da kansa a Zabura ya ce,‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,“Zauna a damana,

43. Sai na sa ka take maƙiyanka.” ’

44. Dawuda ya ce shi Ubangiji ne. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?”

45. Ya ce wa almajiransa a gaban dukan jama'a,

Luk 20