Luk 20:20-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Sai suka yi ta haƙwansa, suka aiki 'yan rahoto, su kuwa suka nuna kamar su masu adalci ne, da nufin su kama shi a maganarsa, su kuma ba da shi ga mai mulki ya hukunta shi.

21. Suka tambaye shi suka ce, “Malam, ai, mun sani maganarka da koyarwarka duk gaskiya ne. Ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi.

22. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa babu?”

23. Shi kuwa ya gane makircinsu, ya ce musu,

Luk 20