31. Da ka shirya a gaban kabilai duka,
32. Haske mai bayyana wa alummai hanyarka,Da kuma ɗaukakar jama'arka Isra'ila.”
33. Uwa tasa da ubansa kuwa suna mamakin abin da aka faɗa game da shi,
34. Sai Saminu ya sa musu albarka, ya ce wa Maryamu uwar Yesu,“Kin ga wannan yaro, shi aka sa ya zama sanadin faɗuwar waɗansu, tashin waɗansu kuma da yawa cikin Isra'ila,Zai kuma zama alama wadda ake kushenta,