16. Sai suka tafi da hanzari, suka sami Maryamu da Yusufu, da kuma jaririn kwance a komin dabbobi.
17. Da suka gan shi, suka bayyana maganar da aka faɗa musu game da wannan ɗan yaro.
18. Duk waɗanda suka ji kuma, suka yi ta al'ajabin abin da makiyayan nan suka faɗa musu.
19. Maryamu kuwa sai ta riƙe duk abubuwan da aka faɗa, tana biya su a zuci.