Luk 18:32-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Gama za a bāshe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa yau.

33. Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma ya tashi.”

34. Amma ko ɗaya ba su fahimci waɗannan abubuwa ba, domin zancen nan a ɓoye yake daga gare su, ba su ma gane abin da aka faɗa ba.

35. Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara.

36. Da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko mene ne.

Luk 18