23. Da jin haka, sai ya yi baƙin ciki gaya, don shi mai arziki ne da gaske.
24. Yesu kuwa da ya gan shi haka, ya ce, “Kai! Da ƙyar kamar me masu dukiya su shiga Mulkin Allah!
25. Ai, zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.”
26. Waɗanda suka ji wannan magana suka ce, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?”
27. Amma Yesu ya ce, “Abin da ya fi ƙarfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
28. Sai Bitrus ya ce, “To, ai, ga shi, mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
29. Yesu ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda Mulkin Allah,
30. sa'an nan ya kasa samun ninkinsu mai yawa a yanzu, a Lahira kuma ya sami rai madawwami.”