Luk 15:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. To, sai duk masu karɓar haraji da masu zunubi suka yi ta matsowa wurinsa su saurare shi.

2. Sai Farisiyawa da malaman Attaura suka riƙa gunaguni suna cewa, “Haba! Wannan mutum yana karɓar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci!”

3. Sai ya ba su wannan misali ya ce.

4. “In waninku yana da tumaki ɗari, ɗayarsu ta ɓace, to, ba sai ya bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta ɓata, har ya same ta ba?

Luk 15