14. Wata rana Yesu yana fitar da beben aljan. Da aljanin ya fita, sai beben ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki.
15. Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Ba'alzabul sarkin aljannu yake fitar da aljannu.”
16. Waɗansu kuwa, don su gwada shi, suka nema ya nuna musu wata alama daga Sama.