29. Amma ta damu ƙwarai da maganar, ta yi ta tunani ko wannan wace irin gaisuwa ce.
30. Mala'ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31. Ga shi kuma, za ki yi ciki, ki haifi ɗa, ki kuma sa masa suna Yesu.
32. Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki.Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda,