Luk 1:29-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Amma ta damu ƙwarai da maganar, ta yi ta tunani ko wannan wace irin gaisuwa ce.

30. Mala'ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.

31. Ga shi kuma, za ki yi ciki, ki haifi ɗa, ki kuma sa masa suna Yesu.

32. Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki.Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda,

Luk 1