Luk 1:15-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Domin zai zama mai girma a wurin Ubangiji,Ba kuwa zai sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba.Za a cika shi da Ruhu Mai TsarkiTun yana cikin uwa tasa.

16. Zai kuma juyo da Isra'ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu.

17. Zai riga shi gaba cikin ruhu da iko irin na Iliya.Yă mai da hankalin iyaye a kan 'ya'yansu,Yă kuma juyo da marasa biyayya su bi hikimar adalai,Ya tanada wa Ubangiji jama'a, ya same su a shirye.”

18. Sai Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta ƙaƙa zan san haka? Ga ni tsoho, maiɗakina kuma ta kwana biyu.”

19. Sai mala'ikan ya amsa ya ce, “Ni ne Jibra'ilu da yake tsaye a gaban Allah. An aiko ni ne in yi maka magana, in kuma yi maka wannan albishir.

Luk 1