9. Amma itacen zaitun ya ce musu, ‘In bar maina wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in tafi in yi ta fama da itatuwa?’
10. Sai kuma itatuwa suka ce wa itacen ɓaure, ‘Ka zo, ka zama sarkinmu.’
11. Amma itacen ɓaure ya ce musu, ‘In bar kyawawan 'ya'yana masu zaƙi, don in tafi in yi ta fama da itatuwa?’
12. Itatuwa kuma suka ce wa kurangar inabi, ‘Ki zo, ki mallake mu.’
13. Sai kurangar inabi ta ce, ‘In bar ruwan inabina wanda yake faranta zuciyar allolin da ta mutane, don in tafi, in yi ta fama da itatuwa?’
14. Sa'an nan dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo, ka zama sarkinmu.’
15. Itacen ƙaya kuwa ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske kuke, kuna so ku naɗa ni sarkinku, to, sai ku zo, ku fake a inuwata, in ba haka ba kuwa, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al'ul na Lebanon.’ ”