L. Mah 15:9-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Filistiyawa suka haura, suka kafa sansani a Yahudiya, suka bazu a cikin Lihai.

10. Mutanen Yahuza suka ce, “Me ya sa kuka kawo mana yaƙi?”Filistiyawa suka ce, “Mun zo ne domin mu kama Samson, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”

11. Sa'an nan mutum dubu uku na Yahuza suka gangara zuwa kogon dutsen Itam. Suka ce wa Samson, “Ba ka sani ba Filistiyawa ne suke mulkinmu? Me ya sa ka yi mana haka?”Shi kuwa ya amsa musu, ya ce, “Kamar yadda suka yi mini, haka ni kuma na yi musu.”

L. Mah 15