L. Kid 4:18-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. “Kada ku bar zuriyar Kohat

19. ta hallaka ta wurin kusatar waɗannan tsarkakakkun abubuwa. Maganin abin, shi ne sai Haruna da 'ya'yansa maza, su shiga, su nuna wa kowannensu irin aikin da zai yi, da kayan da zai ɗauka.

20. Amma idan Kohatawa suka shiga alfarwar suka tarar firistoci suna shisshirya tsarkakakkun abubuwa don tashi, har dai in sun gani, to za su mutu.”

21. Ubangiji ya kuma faɗa wa Musa,

22. ya ƙidaya 'ya'yan Gershon, maza, bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu

23. ya rubuta su tun daga mai shekara talatin, har zuwa mai shekara hamsin, duk wanda ya isa yin aikin da zai yi a alfarwa ta sujada.

24. Wannan shi ne aikin da iyalan Gershonawa za su yi wajen ɗaukar kaya.

25. Za su ɗauki alfarwa ta sujada, da labule na ciki da na waje, da murfi na fatun tumaki wanda yake a bisa alfarwar, da kuma labulen ƙofar alfarwa ta sujada,

L. Kid 4