L. Kid 26:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Bayan annobar, sai Ubangiji ya ce wa Musa da Ele'azara, ɗan Haruna, firist,

2. “Ku ƙidaya dukan taron jama'ar Isra'ila tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba bisa ga gidajen ubanninsu. Ku ƙidaya duk wanda ya isa zuwa yaƙi a cikin Isra'ilawa.”

3. Sai Musa da Ele'azara, firist, suka yi musu magana a filayen Mowab daura da Yariko, suka ce,

4. “A ƙidaya mutane tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba kamar yadda Ubangiji ya umarta.”Isra'ilawa waɗanda suka fita daga ƙasar Masar ke nan.

5. Ra'ubainu shi ne ɗan fari na Yakubu. 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, su ne Hanok, da Fallu,

6. da Hesruna, da Karmi.

7. Waɗannan yawansu ya kai dubu arba'in da uku da ɗari bakwai da talatin (43,730).

L. Kid 26