L. Kid 16:21-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. “Ku ware kanku daga cikin taron jama'ar nan, ni kuwa in hallaka su nan take.”

22. Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki, suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin 'yan adam duka, za ka yi fushi da dukan taron jama'a saboda zunubin mutum ɗaya?”

23. Sai Ubangiji ya ce wa Musa,

24. “Ka faɗa wa jama'a su tashi, su nisanci alfarwar Kora, da ta Datan, da ta Abiram.”

L. Kid 16