4. Ku roƙi shugaban kowace kabila ya taimake ku.”
5-15. Waɗannan su ne mutanen da aka zaɓa. Kabila Shugaban Kabila Ra'ubainu Elizur ɗan Shedeyur Saminu Shelumiyel ɗan Zurishaddai Yahuza Nashon ɗan Amminadab Issaka Netanel ɗan Zuwar Zabaluna Eliyab ɗan Helon Ifraimu Elishama ɗan Ammihud Manassa Gamaliyel ɗan Fedazur Biliyaminu Abidan ɗan Gideyoni Dan Ahiyezer ɗan Ammishaddai Ashiru Fagiyel ɗan Okran Gad Eliyasaf ɗan Deyuwel Naftali Ahira ɗan Enan
16. Waɗannan shugabannin kabilai waɗanda suke manya cikin kabilansu, an zaɓe su daga cikin jama'a domin wannan aiki.
17. Musa da Haruna suka ɗauki waɗannan mutane goma sha biyu,
18. suka kuma kira dukan jama'a wuri ɗaya a ran ɗaya ga watan biyu. Dukan mutanen kuwa aka rubuta su bisa ga kabilansu da iyalansu, da kuma sunayen dukan mazaje masu shekara ashirin ko fi, duk aka ƙidaya su aka rubuta,
19. kamar yadda Ubangiji ya umarta.Musa ya rubuta jama'a a jeji ta Sinai.
47. Amma ba a rubuta Lawiyawa tare da sauran kabilai ba,
48. gama Ubangiji ya ce wa Musa,
49. “Sa'ad da kake ƙidaya Isra'ilawa, kada ka haɗa da kabilar Lawi.
50. A maimakon haka, sai ka sa Lawiyawa su zama masu lura da alfarwa ta sujada da kayayyakinta. Za su ɗauki alfarwar da kayayyakinta, su yi aikinta, a zango kuma sai su sauka kewaye da ita.