L. Fir 25:32-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Amma a kan biranen Lawiyawa, da gidajen da suke cikin biranen da suka mallaka, Lawiyawa suna da izini su fanshe su a kowane lokaci.

33. Amma idan wani daga cikin Lawiyawa bai fanshi gidansa ba, a shekara ta hamsin ta murna sai a mayar masa da gidan nan na cikin birnin da suka mallaka, gama gidajen da suke cikin biranen Lawiyawa su ne nasu rabo a cikin Isra'ilawa.

34. Ba za a jinginar da hurumin biranensu ba, gama wannan shi ne abin mallakarsu har abada.”

35. “Idan ɗan'uwanka, Ba'isra'ile, ya talauce, ya kasa riƙon kansa, sai ka riƙe shi kamar baƙon da yake baƙunci a wurinka.

L. Fir 25