L. Fir 23:30-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Duk kuma wanda ya yi aiki a wannan rana, Ubangiji kansa zai kashe shi.

31. Wannan ka'ida ta shafi dukan zuriyarsu a duk inda suke.

32. Daga faɗuwar ranar tara ga watan, har zuwa faɗuwar ranar goma ga watan, su kiyaye wannan ta zama ranar hutu musamman. A wannan lokaci ba wanda zai ci abinci.

33. Ubangiji kuma ya yi magana da Musa, ya ce ya faɗa wa Isra'ilawa, cewa,

34. a rana ta goma sha biyar ga watan bakwai za a yi Idin Bukkoki kwana bakwai saboda Ubangiji.

35. Za a yi muhimmin taro na sujada a rana ta fari. Ba za su yi aiki ba.

36. A kwana bakwai ɗin za su riƙa miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. A rana ta takwas kuma sai su yi muhimmin taro na sujada, su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Rana ce ta yin sujada, kada su yi aiki.

L. Fir 23