L. Fir 23:28-34 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Ba za su yi aiki a wannan rana ba, gama rana ce ta yin kafara dominsu.

29. Duk wanda ya ci abinci a wannan rana ba za a lasafta shi ɗaya daga cikin jama'ar Allah ba.

30. Duk kuma wanda ya yi aiki a wannan rana, Ubangiji kansa zai kashe shi.

31. Wannan ka'ida ta shafi dukan zuriyarsu a duk inda suke.

32. Daga faɗuwar ranar tara ga watan, har zuwa faɗuwar ranar goma ga watan, su kiyaye wannan ta zama ranar hutu musamman. A wannan lokaci ba wanda zai ci abinci.

33. Ubangiji kuma ya yi magana da Musa, ya ce ya faɗa wa Isra'ilawa, cewa,

34. a rana ta goma sha biyar ga watan bakwai za a yi Idin Bukkoki kwana bakwai saboda Ubangiji.

L. Fir 23