28. Ba za su yi aiki a wannan rana ba, gama rana ce ta yin kafara dominsu.
29. Duk wanda ya ci abinci a wannan rana ba za a lasafta shi ɗaya daga cikin jama'ar Allah ba.
30. Duk kuma wanda ya yi aiki a wannan rana, Ubangiji kansa zai kashe shi.
31. Wannan ka'ida ta shafi dukan zuriyarsu a duk inda suke.
32. Daga faɗuwar ranar tara ga watan, har zuwa faɗuwar ranar goma ga watan, su kiyaye wannan ta zama ranar hutu musamman. A wannan lokaci ba wanda zai ci abinci.
33. Ubangiji kuma ya yi magana da Musa, ya ce ya faɗa wa Isra'ilawa, cewa,
34. a rana ta goma sha biyar ga watan bakwai za a yi Idin Bukkoki kwana bakwai saboda Ubangiji.