17. ya faɗa wa Haruna cewa, “Kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani ya kusato garin ya miƙa hadaya ta ci gare ni har abada.
18. Duk mutumin da yake da lahani na makanta, ko gurguntaka, ko rauni a fuska, ko gaɓar da ta fi wata,
19. ko tauyayye a ƙafa ko a hannu,
20. ko mai ƙusumbi, ko wada, ko mai lahani a ido, ko cuta mai sa ƙaiƙayi, ko kirci, ko dandaƙaƙƙe, ba zai kusato garin ya miƙa hadaya ba.