L. Fir 16:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Ubangiji ya yi magana da Musa bayan rasuwar 'ya'yan Haruna, maza biyu, sa'ad da suka hura wuta marar tsarki a gaban Ubangiji, suka mutu.

2. Ubangiji kuma ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan'uwanka Haruna kada ya riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule ko yaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada ya mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.

3. Amma sai Haruna ya shiga Wuri Mafi Tsarki bayan da ya kawo ɗan bijimi domin yin hadaya don zunubi, da rago don yin hadaya ta ƙonawa.”

L. Fir 16