L. Fir 15:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ba Musa da Haruna waɗannan ka'idodi

2. domin jama'ar Isra'ila. Duk lokacin da wani namiji yake ɗiga daga al'aurarsa, ƙazantacce ne.

3. Ko al'aurar tana ɗiga ko ta daina shi dai ƙazantacce ne.

4. Kowane gado da mai ɗigan ya kwanta a kai ya ƙazantu, da kowane abu da ya zauna a kai ya ƙazantu.

5. Duk wanda ya taɓa gadonsa, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice.

L. Fir 15