3. Gama kun mutu, ranku kuwa a ɓoye yake a gun Almasihu cikin Allah.
4. Sa'ad da Almasihu wanda yake shi ne ranmu ya bayyana, sai ku ma ku bayyana tare da shi a cikin ɗaukaka.
5. Saboda haka, sai ku kashe zukatanku ga sha'awace-sha'wacen duniya, wato fasikanci, da aikin lalata, da muguwar sha'awa, da mummunan buri, da kuma kwaɗayi, wanda shi ma bautar gumaka ne.
6. Saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake sauka a kan kangararru.
7. A dā kuna bin waɗannan sa'ad da suke jiki a gare ku.