K. Mag 8:22-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. “Ni ce halittar farko da UbangijiYa fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni.

23. Da farkon farawa ni aka fara halittawaKafin a yi duniya.

24. Ni aka fara yi kafin tekuna,A sa'ad da ba maɓuɓɓugan ruwa.

25. Ni aka fara yi kafin a yi duwatsu,Kafin a kafa tuddai a wurarensu,

26. Kafin Allah ya halicci duniya da filayenta,Ko ɗan ɓarɓashin ƙasa.

27. A can nake sa'ad da ya shata sararin sama,Da sa'ad da ya shimfiɗa al'arshi a hayin tekuna,

28. Da sa'ad da ya sa gizagizai a sararin sama,Ya buɗe maɓuɓɓugan teku,

29. Ya kuma umarci ruwan teku, kada ya zarce wurin da ya sa.Ina can sa'ad da ya kafa harsashin ginin duniya.

30. Ina kusa da shi kamar mai tsara fasalin gini,Ni ce abar murnarsa kowace rana,A ko yaushe ina farin ciki a gabansa.

31. Ina farin ciki da duniya,Ina murna da 'yan adam.

32. “Yanzu ku matasa, ku kasa kunne gare ni,Ku yi abin da na ce, za ku yi farin ciki.

K. Mag 8