K. Mag 8:18-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Ina da dukiya da daraja da zan bayar,Da wadata da nasara kuma.

19. Abin da za ka samu daga gare niYa fi zinariya kyau, da azurfa tsantsa.

20. A kan hanyar adalci nake tafiya,Rankai a kan hanyoyin gaskiya.

21. Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata,Ina kuma cika gidajensu da wadata.

22. “Ni ce halittar farko da UbangijiYa fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni.

23. Da farkon farawa ni aka fara halittawaKafin a yi duniya.

24. Ni aka fara yi kafin tekuna,A sa'ad da ba maɓuɓɓugan ruwa.

25. Ni aka fara yi kafin a yi duwatsu,Kafin a kafa tuddai a wurarensu,

26. Kafin Allah ya halicci duniya da filayenta,Ko ɗan ɓarɓashin ƙasa.

27. A can nake sa'ad da ya shata sararin sama,Da sa'ad da ya shimfiɗa al'arshi a hayin tekuna,

28. Da sa'ad da ya sa gizagizai a sararin sama,Ya buɗe maɓuɓɓugan teku,

29. Ya kuma umarci ruwan teku, kada ya zarce wurin da ya sa.Ina can sa'ad da ya kafa harsashin ginin duniya.

30. Ina kusa da shi kamar mai tsara fasalin gini,Ni ce abar murnarsa kowace rana,A ko yaushe ina farin ciki a gabansa.

31. Ina farin ciki da duniya,Ina murna da 'yan adam.

32. “Yanzu ku matasa, ku kasa kunne gare ni,Ku yi abin da na ce, za ku yi farin ciki.

33. Ku saurari abin da aka koya muku,Ku zama masu hikima, kada ku yi sakaci da ita.

34. Mutumin da ya kasa kunne gare ni, zai yi farin ciki haka nan,Wato yakan tsaya a ƙofata ko yaushe,Yana kuma jira a ƙofar shiga gidana.

35. Mutumin da ya same ni ya sami rai,Ubangiji zai ji daɗinsa.

36. Mutumin da bai same ni ba ya cuci kansa,Duk wanda yake ƙina mutuwa yake ƙauna.”

K. Mag 8