12. Ni ce hikima, ina da basira,Ina da ilimi da faɗar daidai.
13. Ƙin mugunta shi ne tsoron Ubangiji,Na ƙi girmankai, da fāriya, da mugayen hanyoyi,Da maganganu na ƙarya.
14. Nakan shirya abin da zan yi, in kuwa yi shi.Ina da fahimi, ina da ƙarfi.
15. Nakan taimaki sarakuna su yi mulki,Mahukunta kuma su tsara dokoki masu kyau.
16. Kowane mai mulki a duniya, da taimakona yake mulki,Ƙusoshin hukumomi da dattawan gari duka ɗaya.
17. Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata,Dukan wanda yake nemana kuma zai same ni.
18. Ina da dukiya da daraja da zan bayar,Da wadata da nasara kuma.
19. Abin da za ka samu daga gare niYa fi zinariya kyau, da azurfa tsantsa.
20. A kan hanyar adalci nake tafiya,Rankai a kan hanyoyin gaskiya.
21. Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata,Ina kuma cika gidajensu da wadata.