31. duk da haka in an kama shi, sai ya biya diyya sau bakwai, tilas kuwa ya ba da dukan abin da yake da shi.
32. Amma mazinaci marar hankali ne, gama hallaka kansa yake yi.
33. Zai sha dūka, a wulakanta shi, zai dawwama cikin kunya.
34. Hasalar miji mai kishi babu irinta, ramawarsa ba dama.
35. Ba zai karɓi biya ba, ba kyautar da za a yi masa wadda za ta kwantar da fushinsa.