24. Za ta tsare ka daga mugayen mata, daga kalmomin alfasha da suke fitowa daga bakin matan waɗansu.
25. Kada kyansu ya jarabce ka, kada ka faɗa cikin tarkon feleƙensu.
26. Mutum ta dalilin karuwa zai sha hasarar abin da ya mallaka duka ta wurin zina.
27. Ka iya rungumar wuta a ƙirjinka sa'an nan ka ce ba za ta ƙone tufafinka ba?
28. Ka iya tafiya a kan garwashi sa'an nan ka ce ƙafafunka ba za su ƙone ba?
29. Haka yake da mutumin da ya kwana da matar wani. Duk wanda ya aikata wannan, zai sha wahala.