K. Mag 6:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ɗana, ka taɓa yin alkawari ka ɗaukar wa wani lamuni?

2. Maganganunka sun taɓa kama ka, ko alkawaranka sun taɓa zamar maka tarko?

3. To, ɗana, kana cikin ikon wannan mutum, amma ga yadda za ka yi ka fita, sheƙa zuwa wurinsa, ka roƙe shi ya sake ka.

4. Kada ka yarda ka yi barci ko ka huta.

5. Ka fita daga cikin tarkon kamar tsuntsu ko barewar da ta tsere wa maharbi.

6. Bari ragwaye su yi koyi da tururuwa.

7. Ba su da shugaba, ba su da sarki, ko mai mulki,

8. amma da kaka sukan tanada wa kansu abinci, domin kwanakin bazara.

16-19. Akwai abu shida, i, har bakwai ma, waɗanda Ubangiji yake ƙi, waɗanda ba zai haƙura da su ba,duban raini,harshe mai faɗar ƙarya,hannuwan da suke kashe marasa laifi,kwanyar da take tunane-tunanen mugayen dabaru,mutum mai gaggawar aikata mugunta,mai yawan shaidar zur,mutum mai ta da fitina a tsakanin abokai.

K. Mag 6