1. Wanda ake ta tsauta wa a kai a kai, amma ya taurare, ba makawa tasa ta ƙare farat ɗaya.
2. Sa'ad da masu adalci suke mulki, jama'a sukan yi murna, amma sa'ad da mugaye suke mulki, jama'a sukan yi nishi.
3. Wanda yake ƙaunar hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa.Amma wanda yake abuta da karuwai zai lalatar da dukiyarsa.