K. Mag 21:10-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Mugaye sun zaƙu su aikata mugunta, ba su yi wa kowa jinƙai.

11. Sa'ad da aka hukunta mai girmankai, ko marar tunani yakan koyi wani abu, mutum mai hikima yakan koyi abin da ake koya masa.

12. Adali ya san tunanin mugaye, yakan kuwa zama sanadin lalacewarsu.

13. Idan ka ƙi jin kukan matalauci, naka kukan da kake yi na neman taimako, ba za a ji ba.

14. Kyauta a asirce takan kwantar da zuciyar wanda yake fushi da kai.

15. Sa'ad da aka yi adalci mutanen kirki sukan yi murna, amma mugaye sukan yi baƙin ciki.

16. Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali.

K. Mag 21