K. Mag 12:2-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Ubangiji yana murna da mutanen kirki, amma yakan hukunta masu shirya mugunta.

3. Mugunta ba ta kawo zaman lafiya, amma adalai sukan tsaya daram.

4. Matar kirki abar fāriya ce, abar murna ga mijinta, amma idan ta sa shi kunya, ta zama masa kamar ciwo a ƙashinsa.

5. Amintattun mutane za su yi maka abin da yake daidai, amma mugaye za su ruɗe ka.

6. Maganganun mugaye na kisankai ne, amma kalmomin adalai sukan ceci waɗanda ake neman ransu.

7. Mugaye sukan gamu da faɗuwarsu, ba magāda, amma iyalan adalai sukan dawwama.

8. Idan kai haziƙi ne, za a yabe ka, amma idan kai dakiki ne, mutane za su raina ka.

K. Mag 12