1. Mutumin da yake ƙaunar ilimi yakan so a faɗa masa kuskurensa, wauta ce mutum ya ƙi yarda a faɗa masa laifinsa.
2. Ubangiji yana murna da mutanen kirki, amma yakan hukunta masu shirya mugunta.
3. Mugunta ba ta kawo zaman lafiya, amma adalai sukan tsaya daram.
4. Matar kirki abar fāriya ce, abar murna ga mijinta, amma idan ta sa shi kunya, ta zama masa kamar ciwo a ƙashinsa.
5. Amintattun mutane za su yi maka abin da yake daidai, amma mugaye za su ruɗe ka.
6. Maganganun mugaye na kisankai ne, amma kalmomin adalai sukan ceci waɗanda ake neman ransu.