1. Aka rufe Yariko ciki da waje, ba mai fita, ba mai shiga saboda Isra'ilawa.
2. Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “Duba, na ba da Yariko, da sarkinta, da jarumawanta a hannunka.
3. Kai da dukan mayaƙa za ku zagaya birnin sau ɗaya kowace rana har kwana shida.