Josh 18:18-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Sai ta wuce ta yi arewa daura da gefen Bet-araba, daga nan ta gangara zuwa Araba.

19. Ta kuma zarce zuwa arewa daura da gefen Bet-hogla, ta tsaya a arewacin gaɓar Tekun Gishiri a ƙarshen Urdun wajen kudu.

20. Kogin Urdun shi ne iyakar a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Biliyaminu suka gāda.

21. Biranen iyalan kabilar Biliyaminu ke nan Yariko, da Bet-hogla, da Emekkeziz,

22. da Bet-araba, da Zemarayim, da Betel,

23. da Awwim, da Fara, da Ofra,

24. da Kefar-ammoni, da Ofni, da Geba. Birane goma sha biyu ke nan tare da ƙauyukansu.

25. Akwai kuma Gibeyon, da Rama, da Biyerot,

26. da Mizfa, da Kefira, da Moza,

27. da Rekem, da Irfeyel, da Tarala,

Josh 18