Ish 9:6-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ga shi, an haifa mana ɗa!Mun sami yaro!Shi zai zama Mai Mulkinmu.Za a kira shi, “Mashawarci Mai Al'ajabi,”“Allah Maɗaukaki,”“Uba Madawwami,”“Sarkin Salama.”

7. Sarautar ikonsa za ta yi ta ci gaba,Mulkinsa zai kasance da salama kullayaumin,Zai gāji sarki Dawuda, ya yi mulki a matsayinsa,Zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya,Tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani.Ubangiji Mai Runduna ne ya yi niyyar aikata wannan duka.

8. Ubangiji ya hurta hukunci a kan mulkin Isra'ila, da a kan zuriyar Yakubu.

Ish 9