Ish 29:22-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda ya fanshi Ibrahim daga wahala, ya ce, “Jama'ata, ba za a ƙara kunyatar da ku ba, fuskokinku ba za su ƙara yanƙwanewa don kunya ba.

23. Za ku ga 'ya'yan da zan ba ku, sa'an nan ne za ku tabbatar, cewa ni ne Allah Mai Tsarki na Isra'ila. Za ku girmama ni, ku yi tsorona.

24. Wawaye za su koya su gane, waɗanda a kullum sai gunaguni suke yi, za su yi murna su koya.”

Ish 29