Irm 9:10-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Zan yi kuka in yi kururuwa sabodatsaunuka,Zan yi kuka saboda wuraren kiwo,Domin sun bushe sun zama marasaamfani.Ba wanda yake bi ta cikinsu.Ba a kuma jin kukan shanu,Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudusun tafi.

11. “Ni Ubangiji na ce, zan mai daUrushalima tsibin kufai,Wurin zaman diloli,Zan kuma mai da biranen Yahuzakufai, inda ba kowa.”

12. Wa yake da isasshiyar hikimar da zai fahimci wannan? Wa Ubangiji ya faɗa masa don ya sanar? Me ya sa ƙasar ta lalace ta zama kufai, har ba wanda yake iya ratsa ta, kamar hamada?

Irm 9