27. Ku kashe dukan bijimanta, a kai sumayanka!Kaitonsu, gama kwanansu ya ƙare,Lokacin hukuncinsu ya yi.
28. Ku ji, sun gudu sun tsere daga ƙasarBabila,Don su faɗa cikin Sihiyona,Sakayyar Ubangiji Allahnmu dominHaikalinsa.
29. “Ku kirawo 'yan baka, dukanwaɗanda sukan ja baka, su faɗawa Babila.Ku kafa sansani kewaye da ita, kadaku bar kowa ya tsira.Ku sāka mata bisa ga dukanayyukanta, gama ta raina UbangijiMai Tsarki na Isra'ila.