Irm 29:10-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. “Ubangiji ya ce, ‘Sa'ad da kuka cika shekara saba'in a Babila, zan ziyarce ku, zan kuwa cika muku alkawarina. Zan komo da ku zuwa wannan wuri.

11. Gama na san irin shirin da na yi muku, ni Ubangiji na faɗa. Shirin alheri, ba na mugunta ba. Zan ba ku gabata da sa zuciya.

12. Sa'an nan za ku yi kira a gare ni, ku yi addu'a a wurina, zan kuwa ji ku.

13. Za ku neme ni ku same ni, idan kun neme ni da zuciya ɗaya.

Irm 29