Irm 25:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi wa Irmiya magana a kan dukan mutanen Yahuza. A shekarar da Nebukadnezzar ya ci sarautar Babila,

2. a shekarar ce, annabi Irmiya ya yi wa dukan mutanen Yahuza da dukan mazaunan Urushalima magana cewa,

3. “Shekaru ashirin da uku ke nan tun daga shekara ta goma sha uku ta mulkin Yosiya, ɗan Amon, Sarkin Yahuza, har zuwa yau, Ubangiji ya yi mini magana, ni kuwa na yi ta faɗa muku, amma ba ku ji ba.

19-26. Ga lissafin sauran da za su shaƙoƙon.Fir'auna Sarkin Masar da kumabarorinsa, da sarakunansa,Dukan jama'arsa, da dukanbaƙin da suke tare da su,dukan sarakunan ƙasar Uz,dukan sarakunan ƙasarFilistiyawa, wato Ashkelon, daGaza, da Ekron, da saura naAshdod,Edom da Mowab, da 'ya'yanAmmon maza,dukan sarakunan Taya, da dukansarakunan Sidon,dukan sarakunan da suke gaɓarBahar Rum da waɗanda suke atsibiran tekun,Dedan, da Tema, da Buz, dadukan waɗanda suke yi wakansu sanƙo,dukan sarakunan Arabiya,dukan sarakunan tattarmukanmutane da suke zaune ahamada,dukan sarakunan Zimri, da dukansarakunan Elam, da dukansarakunan Mediya,dukan sarakunan arewa, na nesada na kusa bi da bi.Dukan mulkokin da suke fuskar duniya za su sha daga ciki. Daga nan sai Sarkin Babila a bayansu duka, zai sha nasa.

Irm 25