Irm 18:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,

2. “Ka tashi, ka gangara zuwa gidan maginin tukwane, a can zan yi maka magana.”

3. Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, na iske shi yana ginin tukwane a kan na'urar ginin tukwanen.

4. Abin da yake ginawa ya lalace a hannunsa, sai ya sāke gina wani abu dabam da yumɓu ɗin, yadda ya ga dama.

5. Sa'an nan Ubangiji ya ce mini,

Irm 18