1. Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce,
2. “Ka tashi, ka gangara zuwa gidan maginin tukwane, a can zan yi maka magana.”
3. Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, na iske shi yana ginin tukwane a kan na'urar ginin tukwanen.
4. Abin da yake ginawa ya lalace a hannunsa, sai ya sāke gina wani abu dabam da yumɓu ɗin, yadda ya ga dama.
5. Sa'an nan Ubangiji ya ce mini,