17. Ku tattara kayayyakinku,Ku mazaunan wurin da aka kewayeda yaƙi.
18. Gama haka Ubangiji ya ce,“Ga shi, ina jefar da mazaunanƙasar daga ƙasarsu a wannanlokaci,Zan kawo musu wahala, za su kuwaji jiki.”
19. Tawa ta ƙare, saboda raunin da akayi mini.Raunina mai tsanani ne,Amma na ce, lalle wannan azaba ce,Tilas in daure da ita.
20. An lalatar da alfarwata,Dukan igiyoyi sun tsintsinke,'Ya'yana maza sun bar ni, ba sunan.Ba wanda zai kafa mini alfarwataYa kuma rataya labulena.