Irm 10:11-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.”

12. Shi ne, ta wurin ikonsa ya yi duniya,Ta wurin hikimarsa ya kafa ta,Ta wurin basirarsa kumaya ya shimfiɗasammai.

13. Sa'ad da ya yi murya akan ji ƙuginruwa a cikin sammaiYakan kawo ƙasashi daga ƙurewarduniya,Yakan yi walƙiyoyi saboda ruwansama,Daga cikin taskokinsa yakan kawoiska.

14. Kowane mutum dakiki ne, mararilimi,Kowane maƙerin zinariya zai shakunya saboda gumakansa,Gama siffofinsa ƙarya ne,Ba numfashi a cikinsu.

15. Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne,A lokacin da za a hukunta su za sulalace.

16. Gama shi ba kamar waɗannan yakeba,Shi na Yakubu ne.Shi ne ya yi dukan kome,Kabilan Isra'ilawa gādonsa,Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

17. Ku tattara kayayyakinku,Ku mazaunan wurin da aka kewayeda yaƙi.

18. Gama haka Ubangiji ya ce,“Ga shi, ina jefar da mazaunanƙasar daga ƙasarsu a wannanlokaci,Zan kawo musu wahala, za su kuwaji jiki.”

Irm 10