Hab 3:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Daga Edom Allah ya zo,Daga dutsen Faran Mai Tsarki yake tahowa.Ɗaukakarsa ta rufe sammai,Duniya kuwa ta cika da yabonsa.

4. Walƙiyarsa kamar hasken rana ce,Haske yana haskakawa daga gare shi,A nan ne ya lulluɓe ikonsa.

5. Annoba tana tafe a gabansa,Cuta kuma tana bin bayansa kurkusa.

6. Ya tsaya, ya auna duniya,Ya duba, sai ya girgiza al'umman duniya.Sa'an nan madawwaman duwatsu suka farfashe,Madawwaman tuddai kuma suka zama bai ɗaya.Haka hanyoyinsa suke tun adun adun.

7. Na ga alfarwan Kushan suna cikin azaba,Labulen ƙasar Madayana suna rawar jiki.

Hab 3