Fit 19:14-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Da Musa ya gangaro daga dutsen zuwa wurin mutane, ya tsarkake su. Su kuwa suka wanke tufafinsu.

15. Sai Musa ya ce musu, “Ku shirya saboda rana ta uku, kada ku kusaci mace.”

16. A safiyar rana ta uku aka yi tsawa, da walƙiyoyi, da girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama'ar da suke cikin zango suka yi rawar jiki.

Fit 19